Kamaru: Jirgin kasa ya kashe mutane da dama

Asalin hoton, Camer 24
Lamarin ya ritsa da mutane da dama
Akalla mutane goma ne suka rasa rayukansu bayan da wani jirgin kasa ya yi hadari a Kamaru.
Kamfanin kula da zirga-zirgar jiragen sama na kasar ya ce hadarin ya faru ne a tsakanin biranen Yaounde da Douala.
Wakilin BBC a kasar ya ce mutane da dama sun samu raunuka a hadarin.
Ya ce motocin daukar marasa lafiya sun wurin da lamarin ya faru a Eseka - wanda ke tsakanin Yaounde da Douala.
Hotunan da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda mutane suka makale a tsakankanun taragun jiragen.
Rahotanni sun ce an kara yawan taragun jiragen saboda an rufe babbar hanyar da ta hada garuruwan biyu sakamakon rugujewar wata gada.