Kamaru: Jirgin kasa ya kashe mutane da dama

Hadarin jirgin kasa a Kamaru

Asalin hoton, Camer 24

Bayanan hoto,

Lamarin ya ritsa da mutane da dama

Akalla mutane goma ne suka rasa rayukansu bayan da wani jirgin kasa ya yi hadari a Kamaru.

Kamfanin kula da zirga-zirgar jiragen sama na kasar ya ce hadarin ya faru ne a tsakanin biranen Yaounde da Douala.

Wakilin BBC a kasar ya ce mutane da dama sun samu raunuka a hadarin.

Ya ce motocin daukar marasa lafiya sun wurin da lamarin ya faru a Eseka - wanda ke tsakanin Yaounde da Douala.

Hotunan da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda mutane suka makale a tsakankanun taragun jiragen.

Rahotanni sun ce an kara yawan taragun jiragen saboda an rufe babbar hanyar da ta hada garuruwan biyu sakamakon rugujewar wata gada.