Kenya ta dauki matakin hana satar amsa

A makon gobe ne ake sa ran za a soma babbar jarrabawar kasar

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

A makon gobe ne ake sa ran za a soma babbar jarrabawar kasar

Hukumomin ilimi na kasar Kenya sun kaddamar da wasu sababbin dokoki da zummar hana dalibai satar amsa a lokutan jarrabawa.

Satar amsa dai ta yi kamari a kasar ta Kenya a shekarun baya bayan nan.

Wata sanar da hukumar ilimin kasar ta fitar ta ce za a daina barin dalibai suna yin amfani da raskwana da alluna a lokutan jarrabawa.

Kazalika an haramta shiga dakin jarrabawa da wayar salula.

Hukumomin sun kara da cewa za a sanya ido kan shugabannin makarantu da malamai domin tabbatar da cewa ba sa taimakawa dalibai wajen satar amsa.

A farkon wannan shekarar dai an rusa majalisar da take lura da jarrabawar kasar bayan an gano wata cuwa-cuwa kan yadda aka shirya jarrabawar sakandare ta shekarar 2015, lamarin da ya sa aka soke sakamon jarrabawa na dalibai 5,000.

A makon gobe ne ake sa ran za a soma babbar jarrabawar kasar.