APC da INEC sun yi mana magudi a Ondo — PDP

Jam'iyyar PDP ta zama mai adawa a Najeriya
Jam'iyyar adawa a Najeriya, PDP ta ce ba ta amince da sakamakon zaben da aka gudanar a jihar Ondo, a karshen makon nan ba.
Jam'iyyar ta kuma zargi Hukumar Zaben Kasar, INEC da hada baki da jam'iyya mai mulki ta APC, a inda PDP ta nemi INEC da ta soke zaben.
A wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na jam'iyyar ta PDP, Prince Dayo Adeyeye, ya fitar, PDP ta ce " sakamakon zaben da wakilin Hukumar Zabe ta INEC, farfesa Abdul-Ganiyu Ambali, ya fitar, yaudara ce sannan kuma bai dace da abun da al'ummar jihar Ondo suka zaba ba".
Sai dai tuntuni hukumar ta INEC ta nesanta kanta daga zarge-zarge irin wanda PDP take yi.
A ranar Lahadi ne dai INEC ta bayyana dan takarar jam'iyyar APC, Rotimi Akeredelu, a matsayin wanda ya lashe zaben jihar ta Ondo.
Mista Dayo ya kara da cewa " abu ne a fili yadda 'yan jam'iyyar APC suka rinka sayen katin zaben mutane a gaban jami'an tsaro".
Daman dai jam'iyyar ta PDP ta yi ta kira ga INEC da ta dage zaben da mako biyu domin sabon dan takararta ya samu zarafin yin kamfe.
A ranar Laraba ne dai kotun daukaka kara, ta ce Eyitayo Jegede na bangaren Ahmed Makarfi ne ya cancanci tsayawa takara, ba Jimoh Ibrahim ba, na bangaren Ali Modu Sheriff.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti Daya Da BBC Na Rana 28/01/2021, Tsawon lokaci 0,57
Minti Daya Da BBC Na Rana 28/01/2021