Nigeria: APC da PDP na fafatawa a zaben Rivers

Asalin hoton, Premium Times
Ba a ga-mu-ciji tsakanin Rotimi Amaechi da Nyesom Wike
Manyan jam'iyyu biyu da ke hamayya da juna a Najeriya na fafata wa a zabukan cike gurbi na 'yan majalisun jiha da tarayya a jihar Rivers.
Jam'iyyar PDP mai mulkin jihar, wacce ta lashe zabukan a baya, kafin daga bisani kotu ta soke, na kokarin sake samun nasara.
Yayin da jam'iyyar APC mai mulkin kasar, amma 'yar adawa a jihar, ke ganin cewa za ta iya kai labari.
Jihar Rivers ta sha fama da rikicin siyasa wanda ke kara kaimi saboda takun-saka tsakanin tsohon gwamnan jihar Rotimi Amaechi da kuma mai ci Nyesom Wike.
Za a yi zabukan ne cikin zaman dar-dar domin kusan sau uku ke nan ake sa rana amma ana dagawa saboda dalilan rashin tsaro.
Sai dai a wannan karon hukumomi sun ce sun shirya inda aka tsaurara matakan tsaro a jihar baki daya.
Ko a ranar Juma'a sai da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi kiran da a kwantar da hankali, yana mai cewa "ba batu ne na a mutu ko a yi rai ba."
'Yan majalisu 22 za a zaba a zabukan na ranar Asabar da suka hada da na majalisar dattawa da ta wakillai da kuma jiha.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti Daya Da BBC na Rana 27/01/2021, Tsawon lokaci 1,03
Minti Daya Da BBC na Rana 27/01/2021