'Yan sanda a Afirka ta Kuda na kashe 'yan ci rani daga Najeriya

South Africa

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Jami'an Nageriya na zargin 'yan sandan Afirka ta Kuda da kisa

Mai taimaka wa shugaban Najeriya a kan kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa, ta ce an kashe 'yan kasar 116, a Afirka ta Kudu, ba bisa ka'ida ba, a cikin shekaru biyu.

A wani labari da jaridar Daily Trust ta wallafa, Abike DabiriI-Erewa, ta bayyana hakan ne bayan ganawa da Jakadan Afirka ta Kudu zuwa Najeriya, Lulu Louis Mnguni, a Abuja.

Mrs Erewa ta bayyana cewa 'yan sandan Afirka ta Kudu na kashe kusan mutane bakwai a cikin 10:

''Binciken da aka gudanar na nuna cewa a cikin shekaru biyu da suka wuce, 'yan sanda ne suka yi kashe-kashen''.

Jaridar Premium Times wadda ita ma ta wallafa labarin, ba ta bayyana lokacin da kisan mutane 116 ya faru ba.

Sai dai kuma ta bayyana damuwar Mrs DabiriI-Erewa akan yadda ake danganta 'yan ci rani daga Najeriya da aikata laifufuka a Afirka ta Kudu.

''Mun damu musamman ma game da yadda ake danganta duk wani mugun laifi a kan 'yan ci rani daga Najeriya a Afirka ta Kudu. Haka ne, wasu na aikata laifuffuka kuma ya cancanta a hukunta su amma karuwar shari'ar kisa na damun mu matuka."

Kisan dan Najeriya na baya-bayan nan a Afirka ta Kudu ya faru a watan Disambar 2016, a lokacin da 'yan sanda a birnin Cape Town suka shake Victor Nnadi har sai da ya mutu.

Mr Mnguni ya yi alkawari za a bincika kashe-kashen kuma a hukunta wadanda aka samu da laifi.