CAR: Rikici ya sake barkewa a Bangui

Dakarun da aka bincike su sun fito ne daga kasashen Burundi da Gabon

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Dakarun da aka bincike su sun fito ne daga kasashen Burundi da Gabon

Sabon rikici ya sake barkewa a wasu sassan Bangui, babban birnin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

Rahotanni sun ce akalla mutane hudu sun mutu a yankin sojojin sa-kai na PK5, ranar Talata.

Wakilin BBC ya ce, rikicin dai ya barke ne sakamakon kokarin jami'an tsaro na cafke jagoran wata kungiyar sojin kai, a inda mutunin ya yi turjiya.

Daga nan ne kuma aka fara jin tashin harbin bindiga.

Sai dai babu wasu alkaluma daga gwamnati dangane da mutanen da suka mutu kuma ba a iya tantancewa ko har da jagoran kungiyar a cikin mamatan.

Tun dai lokacin da aka hambarar da shugaba Francois Bozize a 2013, rikicin kabilanci da na addini ke barkewa da lafawa.