Niger da Amurka sun dukkufa kan tsaro

Muhammadou Issoufou
Bayanan hoto,

Kasashen Amurka da Nijar za su inganta tsaro har zuwa yankin Sahel

Kwararru ta fannin tsaro na kasashen biyu, Nijar da Amurka na gudanar da taron karfafa matakan tsaro.

Taron bitar na gudana ne a Yamai babban birnin kasar ta Nijar.

Wannan lamari dai zai tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar, da ma sauren kasashen yankin Sahel masu fama da hare-haren ta'adanci.

Kasar Amurka dai na gudanar da wani shiri ne a Afirka, inda take tallafa ma kasashe 6 ta fannin tsaro.

Kasashen sun hada da Nijar da Najeriya da Kenya da Ghana da Mali da kuma Tunisiya.

To sai dai, jama'a mazauna yankunan na kokawa kan sahihancin lamarin tsaro a yankunan, ganin yadda kwalliya bata biyan kudin sabulu.

Daga nashi bangaren kakakin rundunar sojojin kasar Nijar, Kanal Mustapha Ledru, cewa ya yi kwalliya na biyan kudin sabulu,domin babu kasa a duniya, da ke da tsaro dari-bisa-dari a halin da ake ciki yanzu.