Syria: Za mu kawo karshen gwamnatin Assad

Basharul Assad
Bayanan hoto,

Shugaba Assad na Syria ya sha alwashin karbe iko da sauran garuruwan da ke hannun 'yan tawaye

Sabuwar gamayyar kungiyoyin 'yan tawaye na jihadi a kasar Syria, sun ce sun yi niyyar kai mummunan hari kan dakarun gwamnatin kasar.

A watan da ya gabata ne dai aka samae da hadakar kungiyoyin mai suna Hayar Tahrir al-Sham.

Cikin kungiyoyin da suka samar da ita akwai, tsohuwar kungiyar 'yan tawaye ta al-Nusra front mai alaka da kubiyar al-Qaeda.

Kungiyoyin dai sun hade kan su ne a lokacin da aka samu baraka da rarrabuwar kawuna tsakanin wasu daga cikin 'yan tawayen.

A sakon bidiyo na farko da kungiyar ta fitar, da shugabansu Hashem al-Sheikh ya yi magana, ya ce matufar kungiyar da kuma abinda ta sanya a gaba shi ne kawo karshen gwamnatin shugaba Basharul Assad na Syria.

Shekaru biyar kenan ana yaki a kasar ta Syria, tsakanin gwamnati da 'yan tawaye, da kuma kungiyar masu tada kayar baya ta IS mai ikirarin kafa daular musulunci a kasashen Syria da Iraqi.