Limaman da za su jagoranci Sallar Taraweeh da Tahajjud a Masallacin Harami a bana

Asalin hoton, TWITTER/@hsharifain
Hukumomin Saudiyya sun fitar da jerin sunayen limaman da za su jagoranci sallolin Tarawi da Tuhajjud a Masallacin Harami da ke birnin Makka a lokacin azumin bana.
Shafin intanet na Haramain Sharifain ya bayyana cewa limamai shida ne za su jagoranci gudanar da sallolin a bana.
Ana sa ran za a fara Azumin wannan shekarar a cikin watan Afirilu mai zuwa.
Har wa yau, hukumomin Saudiyya sun ce bana babu wasu limamai da za a gayyato domin limancin sallolin, kamar yadda ake gani a shekarun da suka gabata.
Babban limamin masallacin Ka'abah Sheikh Abdul Rahman al-Sudais na daga cikin limaman da hukumomin suka ce za su yi jagorancin sallolin.
Ga hotunan limaman da za su ja ragamar Sallolin Tarawi da Tuhajjud.

Asalin hoton, Alarabiyya News

Asalin hoton, Haramain Sharifain

Asalin hoton, Haramain Sharifain

Asalin hoton, Haramain Sharifain

Asalin hoton, Haramain Sharifain

Asalin hoton, fACEBOOK/Haramain Archives






