An kashe mutum 17 a zanga-zangar adawa da gwamnatin DR Congo

Zanga-zangar adawa da shugaban DR Congo Joseph Kabila

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

Daruruwan mutane ne suka halarci zanga-zangar

Akalla mutane 17 ne suka mutu a zanga-zangar da aka shirya domin tilasta wa Shugaba Joseph Kabila na Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo ya yi murabus.

A cewar ministan cikin gida, Evariste Boshab, uku daga cikin wadanda suka rasa rayukansu 'yan sanda ne, kuma an kona daya ne da ransa.

Masu zanga-zangar sun kafa shingaye, sannan suka farfasa motoci a daya daga cikin manyan hanyoyin Kinshasa, babban birnin kasar.

'Yan sanda sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Wani da ya shaida lamarin ya ce 'yan sandan sun budewa gangamin mutanen wuta.

An ga gawarwakin mutanen da aka kashe a kan tituna bayan kammala zanga-zangar.

Joseph kabila

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

Mista Kabila ya hau mulki a shekarar 2001 bayan an kashe mahaifinsa Laurent Kabila

A ranar Litinin ne aka tsara hukumar zaben kasar za ta sanar da ranar da za a gudanar da zaben shugaban kasa a watan Nuwamba.

Sai dai hukumar ta ce ba zai yiwu a gudanar da shi ba.

'Yan adawa sun ce Mista Kabila na kokarin dakile zaben ne domin ya ci gaba da kasancewa a kan mulki, bayan kammala wa'adinsa a watan Disamba.

A man stands next to a burnt out car after a protest in Kinshasa, Democratic Republic of Congo, Monday, Sept. 19, 2016

Asalin hoton, AP

Bayanan hoto,

Masu zangza-zangar sun kona motoci

policeman with a gun stands in front of anti-riot vehicle

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

An tura 'yan sandan kwantar da tarzoma a kan titunan birnin Kinshasa