Dominic Ongwen ya shaida wa ICC ba shi da laifin yaki

Ongwen

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

Ana zargin Mr Ongwen da kai hari a sansanin 'yan gudun hijira

Kwamandan kungiyar 'yan tawayen LRA da ke Uganda, Dominic Ongwen, ya shaida wa kotun hukunta manyan laifuka ta duniya da ke Hague, ICC bai aikata laifukan yaki ba.

Mr Ongwen ya kara da cewa kungiyar ta LRA ce ke da alhakin aikata laifukan, yana mai cewa ita ce ta sace shi sannan ta sa shi ya zama dan tawaye.

Kungiyar ce ta sace Ongwen, wanda yanzu yake da kusan shekara 40, lokacin yana yaro.

Ana zargin sa da aikata laifukan yaki da na cin zarafin bil adama a Uganda guda 70.

Ana zargin Mr Ongwen da jagorantar 'yan tawaye domin kai hare-hare a sansanonin 'yan gudun hijira guda hudu da ke arewacin Uganda, inda suka kashe tare da gallawa jama'a, kana suka tilasta wa mata aurensu da kuma sanya yara suka zama mayakan kungiyar.

Sai dai ya shaida wa kotun ICC cewa ya kamata a tuhumi kungiyar LRA da shugabanta Joseph Kony, ba shi ba.

line
Dominic Ongwen in the Central African Republic (14 January 2015)

Asalin hoton, Reuters

Dominic Ongwen
Bayanan hoto,

Mr Ongwen ya zama babban kwamandan LRA

Kungiyar LRA ta gallabi tsakiyar Afirka cikin shekara 20

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Kungiyar LRA ta gallabi tsakiyar Afirka cikin shekara 20

'Yan kasar Uganda suna kallon yadda shari'ar ke gudana
Bayanan hoto,

'Yan kasar Uganda suna kallon yadda shari'ar ke gudana