Hankali ya soma kwanciya a Ivory Coast bayan boren soji

Asalin hoton, AFP
An sake bude shaguna a birnin Bouake
Sojoji sun daina boren da suka kwashe kwana biyu suna yi a kasar Ivory Coast inda suke bukatar a ba su alawus.
Mazauna Bouake da kuma masu aiko da rahotanni sun ce babu alamar tashin hankali a kan titunan birnin - kwana daya bayan soji sun kwace ma'aikatar tsaron kasar.
Boren ya bazu zuwa wurare da dama, ciki har da Abidjan, amma hankali ya kwanta a can ma.
A ranar Asabar ne aka sanya hannu a kan wata yarjejeniya tsakanin sojojin da suka yi bore da kuma gwamnati, sai dai babu cikakken bayani kan yarjejeniyar.
Waniwakilin kamfanin dillancin labarai na AFP a Bouake ya ce babu wani rahoton bude wuta a birnin tun ranar Asabar.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, MINTI ƊAYA DA BBC NA RANA 21/01/2021, Tsawon lokaci 1,10
MINTI ƊAYA DA BBC NA RANA 21/01/2021