Buhari zai binciki zabukan 2007 da 2015, Barayin shanu 700 sun tuba a Kaduna
Buhari zai binciki zabukan 2007 da 2015
Gwamnatin Najeriya ta kafa wani kwamiti da zai binciki kamfanin Cambridge Analytica kan ko ya yi katsalandan a zabukan shekarar 2007 da 2015, kamar yadda fadar shugaban kasar ta bayyana.
Cambridge Analytica, wanda yake tattara bayanai kan zabuka, ya tsinci kansa a cikin ce-ce-ku-ce saboda ikirarin da aka yi cewa ya yi amfani da bayanan miliyoyin masu amfani da shafin Facebook domin cimma burin siyasa a kasashen Amurka da Birtaniya.
Asalin hoton, Facebook/Buhari Sallau
Barayin shanu 700 sun tuba a Kaduna
Rundunar 'yan sanda a jihar Kaduna ta Najeriya ta ce ta sasanta da wasu daruruwan 'yan "ta'adda da barayin shanu" da suka addabi jihar.
A 'yan shekarun nan dai ana samun tashin hankali da kashe-kashen jama'a a jihar da ma wadansu jihohi makwabta.
Asalin hoton, AFP
Fulani makiyaya na korafin ana sace musu shanu
An sace amarya da 'yan rakiyarta a jihar Kaduna
Ana ci gaba da alhinin sace wata amarya a kan hanyarta ta zuwa gidan miji a yankin karamar hukumar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna.
Ana zargin masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa ne suka sace amaryar, mai suna Halima, tare da masu yi mata rakiya lokacin da hanya ta biyo da su jihar a kan hanyarsu ta zuwa jihar Neja daga jihar Katsina, bayan an daura aure.
Asalin hoton, Getty Images
Amitabh Bachchan zai fito mai shekara 102 a fim
Shahararren jarumin fina-finan Indiya Amitabh Bachchan, zai fito a matayin mahaifin Rishi Kapoor a wani sabon fim, mai suna "102 Not Out".
Jarumi Amitabh da Rishi Kapoor, za su fito a fim ne tare bayan kwashe shekaru da dama ba a gansu a cikin fim guda ba.
Asalin hoton, Getty Images
Bidiyo: Wace ce Winnie Mandela?
Wace ce Winnie Mandela?
Karanta karin wasu labaran
Domin samun karin bayani da kuma tofa albarkacin bakinku a kan wadannan labaran, sai ku garzaya shafinmu na BBC Hausa Facebook.