Hotunan abin da ya faru a Afirka a makon jiya

Wadansu daga cikin hotunan abubuwan da suka faru a nahiyar Afirka a makon jiya.

An Egyptian dancer performs the Tanoura during the holy fasting month of Ramadan, at el-Ghuri culture Palace in Cairo on May 22, 2018.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wani mawaki lokacin wani taron raye-raye da wake-wake a birnin al-Khahira na kasar Masar

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Raye-rayen suna da farin jini ga al'ummar yankin Gabas ta Tsakiya

Asalin hoton, EPA

Bayanan hoto,

Wadansu masu wake-wake daga kasar Syria lokacin wani taron al'adu a birnin Tunis na kasar Tunusiya ranar Talata

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wadansu kayayyakin tarihi na Masarautar Dahomey wadda take cikin kasar Jamhuriyar Benin a yanzu, a wani gidan adana kayan tarihi da ke birnin Paris na kasar Faransa. Benin ta bukaci a mayar mata da kayayyakin tarihin da aka kai Turai lokacin mulkin mallaka.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

Wani mai sayar da naman daji lokacin da ya rike nama a wata kasuwa a birnin Mbandaka na Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango, birnin yana fama da annubar Ebola.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wata mai fafutikar kare hakkin 'yan luwadi Yvonne Oduor lokacin da take rike da wata tuta a ofishin Majalisar Dinkin Duniya a birnin Nairobi na kasar Kenya

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wani mai goyon bayan Senegal lokacin da yake rike da tutar kasar yayin da yake sauraron sunayen 'yan wasan kasar da za su je Gasar Cin Kofin Duniya wanda za a yi a kasar Rasha

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

Wani dan Ghana Joseph Afrane lokacin da ya yi tsayuwar daukar hoto a birnin Windsor a kasar Birtaniya yayin bikin Gidan Sarautar kasar

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

Wata mai tallan kayan kawa a otel din Windsor Golf da Country Club a birnin Nairobi na kasar Kenya

Asalin hoton, EPA

Bayanan hoto,

Wata 'yar kasar Afirka ta Kudu lokacin da take kallon daurin auren Yarima Harry da Meghan Markle a talabijin a birnin Cape Town ranar Asabar

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wani mutum lokacin da yake karanta wani littafi wanda wani marubuci dan kasar Kwaddibuwa Epiphane Zoro Bi ya rubuta. Littafin yana magana ne game da kabilar yankin Ituri a Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango, inda fiye da mutum 60,000 suka rasa rayukansu.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wani mutum lokacin da yake kokarin kubutar da kayansa daga ambaliyar ruwa a birnin Mogadishu na kasar Somaliya

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

... wannan mutumin ya shiga ambaliyar ruwa ne da taimakon keken jakinsa don ketara hanya

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

Wani yaro lokacin da ya fada cikin ruwa saboda yanayin zafi da ya yi tsanani a birnin Alkhahira na kasar Masar ranar Laraba

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wadansu 'yan Najeriya suna addu'a game da kashe-kashen da ke faruwa a kasar a Legas ranar Talata

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto,

Wata mai tallan kayan kawa Miriam Odemba lokacin da ta halarci taron fina-finan na Cannes Film Festival a kudancin kasar Faransa

Hotuna daga AFP, Getty Images, Reuters da kuma EPA