A nan muka kawo karshen bayanan da muke kawo muku kan rikicin majalisar wakilan Najeriya.
Jibrin ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa
Wakilin BBC ya ce:
'Na hannun daman Dogara'
A baya dai, Abdulmumin Jibril wanda ke wakiltar Kiru da Bebeji a jihar Kano, yana daya daga cikin na hannun damar shugaban majalisar.
Ana bincike kan batun
Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya ta'annati, EFCC da rundunar 'yan sanda da ta farin-kaya sun fara gudanar da bincike kan lamarin bayan Abdulmumini Jibrin ya kai musu koke.
'Zafin kaye ke damunsa'
Sai dai Abdulrazak Namdas, mai magana da yawun majalisar wakilan, ya musanta zarge-zargen da Jibrin ya yi, yana mai cewa zafin cire shi da aka yi daga mumakin shugaban kwamitin kasafin kudi ane ke damunsa.
Getty ImagesCopyright: Getty Images
Dogara ya ce zafin rasa mukami ne ke damun JibrinImage caption: Dogara ya ce zafin rasa mukami ne ke damun Jibrin
Post update
Jibrin ya ce yana da shaidun da ke nuna cewa Dogara, da mataimakinsa Yusuf Lasun, da Alhassan Doguwa da Leo Ogor sun ware wa kansu 40bn a cikin 100bn da aka warewa gaba dayan majalisar dokokin tarayya ta Najeriya.
Asalin rigimar
Rikicin ya barke ne bayan an sauke Abdulmumini Jibrin daga shugabancin kwamitin kasafin kudin majalisar, inda shi kuma ya yi zargin cewa shugaban majalisar Yakubu Dogara da wasu manyan 'yan majalisar uku sun yi cushen kimanin N30bn a kasafin kudin 2016.
BBCCopyright: BBC
Jibrin ya ce dole Dogara ya saukaImage caption: Jibrin ya ce dole Dogara ya sauka
Barkanmu da warhaka
Za mu kawo muku bayanai kan rikicin da yake ci gaba da faruwa a majalisar wakilan Najeriya saboda zargin cushe a kasafin kudin shekarar 2016.
Rahoto kai-tsaye
Daga Nasidi Adamu Yahya da UmmulKhairi Ibrahim
time_stated_uk
Bayyana ra'ayinka
Karshen bayani
A nan muka kawo karshen bayanan da muke kawo muku kan rikicin majalisar wakilan Najeriya.
Jibrin ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa
Wakilin BBC ya ce:
'Na hannun daman Dogara'
A baya dai, Abdulmumin Jibril wanda ke wakiltar Kiru da Bebeji a jihar Kano, yana daya daga cikin na hannun damar shugaban majalisar.
Ana bincike kan batun
Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya ta'annati, EFCC da rundunar 'yan sanda da ta farin-kaya sun fara gudanar da bincike kan lamarin bayan Abdulmumini Jibrin ya kai musu koke.
'Zafin kaye ke damunsa'
Sai dai Abdulrazak Namdas, mai magana da yawun majalisar wakilan, ya musanta zarge-zargen da Jibrin ya yi, yana mai cewa zafin cire shi da aka yi daga mumakin shugaban kwamitin kasafin kudi ane ke damunsa.
Post update
Jibrin ya ce yana da shaidun da ke nuna cewa Dogara, da mataimakinsa Yusuf Lasun, da Alhassan Doguwa da Leo Ogor sun ware wa kansu 40bn a cikin 100bn da aka warewa gaba dayan majalisar dokokin tarayya ta Najeriya.
Asalin rigimar
Rikicin ya barke ne bayan an sauke Abdulmumini Jibrin daga shugabancin kwamitin kasafin kudin majalisar, inda shi kuma ya yi zargin cewa shugaban majalisar Yakubu Dogara da wasu manyan 'yan majalisar uku sun yi cushen kimanin N30bn a kasafin kudin 2016.
Barkanmu da warhaka
Za mu kawo muku bayanai kan rikicin da yake ci gaba da faruwa a majalisar wakilan Najeriya saboda zargin cushe a kasafin kudin shekarar 2016.