Got a TV Licence?

You need one to watch live TV on any channel or device, and BBC programmes on iPlayer. It’s the law.

Find out more
I don’t have a TV Licence.

Rahoto kai-tsaye

Daga Mohammed Abdu

time_stated_uk

  1. Nan muka kawo karshen shirin sai an jiman ku.

  2. An rufe rumfunan zaben kasar Ghana

    An rufe kada kuri'a a zaben kasar Ghana, wanda aka yi na zaben shugaban kasa da na 'yan majalisa na shekarar 2016.

  3. Ana yin zabe cikin kwanciyar hankali a Tamale

    Thomas Naadi

    BBC Africa, Accra

    Ana gudanar da zabe a Tamale da ke Arewacin Ghana cikin kwanciyar hankali.

    Ba a dai samu labarin barkewar rikicin siyasa ba.

    Watakila saboda jami'an tsaro da ke yin sintiri a ciki da wajen birnin ne.

    Zaben Ghana
  4. Yadda ake yin zabe a birnin Kumasi

    Video content

    Video caption: Birnin Kumasi shi ne birnin na biyu mafi girma a kasar ta Ghana bayan Accra,
  5. 'Yan takarar shugaban kasa masu amsa Nana sun yi zabe

    'Yan takarar shugabancin kasar Ghana masu amsa sunan Nana sun kada kuri'arsu a zaben da ake gudanarwa. 

    Daya namiji ne mai amsa sunan Nana Akufo-Addo, shugaban jam'iyar New Patriotic Party, wanda ya yi zabe a birnin Accra. 

    Dayar kuwa mace ce mai suna Nana Konadu Agyeman-Rawlings mai takara a jam'iyar National Democratic Party.    

    Zaben Ghana
    Zaben kasar Ghana
  6. Ana karfafa tsaro a lokacin da ake yin zabe

    Jami'an tsaro da suka hadar da sojoji da yan sanda na ci gaba da sintiri a birnin Kumasi domin tabbatar da tsaro

    Zaben Ghana
    Zaben Ghana
  7. Babu mutane da yawa a mazabar Malaga

    Yusuf Ibrahim Yakasai

    BBC Hausa, Kumasi, Ghana

    A wasu mazabun ba mutane kamar mazabar Malaga.

    To amma a wasu wuraren akwai masu zabe da yawa, kamar mazabar Malam Dudu akwai mutane da dama a kan layi. 

    Kuma babban Jami'in mazabar ya shedawa BBC cewa yana fargabar da wuya za su kammala da masu zabe kafin lokacin da za a kammala kada kuri'a.

    Zaben Ghana
    Zaben Ghana
    Zaben Ghana
  8. Yadda ake zabe da harkar kasuwanci a mazabar Sawaba

    Ibrahim Isa BBC Hausa Accra, Ghana

    Video content

    Video caption: Tun da sanyin safiyar Laraba aka fara kada kuri'a a zaben kasar Ghana
  9. Fursunoni a Ghana na yin zabe a kasar

    Fursunoni suna daga cikin masu kada kuri'a a zaben sugaban kasar Ghana da na 'yan majalissu.

     Wannan shi ne karo na biyu da fursunonin ke yin zabe, bayan wanda suka yi a shekarar 2012. 

     A cewar wata kafar yada labarai da ke Ghana City FM a labarin da ta wallafa a shafinta na Intanet ta ce kimanin fursunoni 2,276 ne aka yi wa rijistar yin zabe a kasar ta Ghana.  

    Zaben Ghana
  10. Yawan mutanen da za su yi zabe

    Ana kada kuri'a ne a mazabu dubu ashirin da takwas da dari tara da casa'in da biyu.

    Haka kuma mutum miliyan goma sha biyar da dubu dari bakwai da uku, da dari tara da casain ne za su kada kuria a zaben shugaban kasar Ghana da na 'yan majalissu.

    Zaben Ghana
  11. Zaben shugaban kasar Ghana da 'yan majalissu

    Zaben Ghana
    Zaben Ghana
  12. Abubuwan da aka yi yakin neman zabe

    Batun tabarbarewar tattalin arziki da kuma cin hanci da rashawa su ne suka mamaye yakin neman zaben.  

    Tattalin arzikin kasar dai ya samu koma baya a 'yan shekarun nan.   

    Video content

    Video caption: Halin da tattalin arzikin Ghana ke ciki
  13. Abubuwa biyar kan zaben Ghana da ya kamata ku sani

    1. Masu suna John sune ke yawan shugabantar kasar

    Tun shekarar 1992 masu suna John ne ke shugabantar kasar.

    2. Tun shekarar 1992, jam'iyyu biyu ne kawai suka mamaye siyasar Ghana. Jam'iyyar National Democratic Congress ce ta shugaba mai mulki. Sai jam'iyyar New Patriotic Party ta hamayya.

    3. A Duk lokacin da jam'iyyar Democrats ta lashe zaben shugaban kasar Amurka..... To sai ka ga Jam'iyyar NDC ma ta ci zabe a Ghana. Kuma idan Republican suka ci a Amurkan, haka ma jam'iyyar NPP ce ke lashe zaben Ghana.

    4. A karon farko a tarihin, an samu mace ta farko Charlotte Osei, wadda ke shugabantar hukumar zaben kasar Ghana. 

    5. Ba a taba samun sauyin gwamnati a Ghana, ba tare da an yi zabe zagaye na biyu ba. 

    Hoton charlotte Osei
    Image caption: Charlotte Osei ce ke shugabantar hukumar da ke kula da zabe a Ghana
  14. Mata masu ciki ba sa bin layin zabe

    Mata masu ciki ba sa bin layi, ana basu dama su kada kuria da zarar sun je rumfar zabe.

    zaben Ghana
  15. An tantance mutane 99 a mazabar Zango B

    Kawo yanzu mutane 99 sun kada kuria a mazabar Zango B, daga cikin mutane 639 kamar yadda wakilin BBC Yusuf Ibrahim Yakasai daga Kumasi a Ghana ya aiko mana da yadda ake tantance masu zabe.

    Video content

    Video caption: Tun da sanyin safiyar Laraba aka fara kada kuri'a
  16. Post update

    Wasu sun kada kuri'a sun koma gida

    Yusuf Ibrahim Yakasai

    BBC Hausa, Kumasi, Ghana

    Tuni wasu yan kasar ta Ghana suka kada kuri'un su kuma suka koma wajen sana'o'in su

    zaben Ghana
  17. Yadda ake tantace mutane a mazabar Zango B

    Yusuf Ibrahim Yakasai

    BBC Hausa, Kumasi, Ghana

    Video content

    Video caption: Tun da safiyar Laraba aka fara yin zabe a Ghana
  18. Wakilin BBC ya kada tasa kuri'ar

    Daya daga cikin ma'aikatan BBC, Akwasi Sarpong, wanda dan kasar ta Ghana ne, kuma a yanzu yana can domin aiko da rahotanni kan zaben, shi ma ya kada tasa kur'ar:

    View more on twitter