An rufe kada kuri'a a zaben kasar Ghana, wanda aka yi na zaben shugaban kasa da na 'yan majalisa na shekarar 2016.
Ana yin zabe cikin kwanciyar hankali a Tamale
Thomas Naadi
BBC Africa, Accra
Ana gudanar da zabe a Tamale da ke Arewacin Ghana cikin kwanciyar hankali.
Ba a dai samu labarin barkewar rikicin siyasa ba.
Watakila saboda jami'an tsaro da ke yin sintiri a ciki da wajen birnin ne.
BBCCopyright: BBC
Yadda ake yin zabe a birnin Kumasi
Video content
Video caption: Birnin Kumasi shi ne birnin na biyu mafi girma a kasar ta Ghana bayan Accra,Birnin Kumasi shi ne birnin na biyu mafi girma a kasar ta Ghana bayan Accra,
'Yan takarar shugaban kasa masu amsa Nana sun yi zabe
'Yan takarar shugabancin kasar Ghana masu amsa sunan Nana sun kada kuri'arsu a zaben da ake gudanarwa.
Daya namiji ne mai amsa sunan Nana Akufo-Addo, shugaban jam'iyar New Patriotic Party, wanda ya yi zabe a birnin Accra.
Dayar kuwa mace ce mai suna Nana Konadu Agyeman-Rawlings mai takara a jam'iyar National Democratic Party.
Jami'an tsaro da suka hadar da sojoji da yan sanda na ci gaba da sintiri a birnin Kumasi domin tabbatar da tsaro
Getty ImagesCopyright: Getty Images
Getty ImagesCopyright: Getty Images
Babu mutane da yawa a mazabar Malaga
Yusuf Ibrahim Yakasai
BBC Hausa, Kumasi, Ghana
A wasu mazabun ba mutane kamar mazabar Malaga.
To amma a wasu wuraren akwai masu zabe da yawa, kamar mazabar Malam Dudu akwai mutane da dama a kan layi.
Kuma babban Jami'in mazabar ya shedawa BBC cewa yana fargabar da wuya za su kammala da masu zabe kafin lokacin da za a kammala kada kuri'a.
BBCCopyright: BBC
BBCCopyright: BBC
BBCCopyright: BBC
Yadda ake zabe da harkar kasuwanci a mazabar Sawaba
Ibrahim Isa BBC Hausa Accra, Ghana
Video content
Video caption: Tun da sanyin safiyar Laraba aka fara kada kuri'a a zaben kasar GhanaTun da sanyin safiyar Laraba aka fara kada kuri'a a zaben kasar Ghana
Fursunoni a Ghana na yin zabe a kasar
Fursunoni suna daga cikin masu kada kuri'a a zaben sugaban kasar Ghana da na 'yan majalissu.
Wannan shi ne karo na biyu da fursunonin ke yin zabe, bayan wanda suka yi a shekarar 2012.
A cewar wata kafar yada labarai da ke Ghana City FM a labarin da ta wallafa a shafinta na Intanet ta ce kimanin fursunoni 2,276 ne aka yi wa rijistar yin zabe a kasar ta Ghana.
Seth Kwame BoatengCopyright: Seth Kwame Boateng
Bin layi domin kada kuri'a
Jami'an zabe na taimakawa masu kada kuri'a hawa kan layi da bin ka'ida a wata mazaba da wakilin BBC Akweasi Sarpong ya ziyarta a birnin Accra:
Ana kada kuri'a ne a mazabu dubu ashirin da takwas da dari tara da casa'in da biyu.
Haka kuma mutum miliyan goma sha biyar da dubu dari bakwai da uku, da dari tara da casain ne za su kada kuria a zaben shugaban kasar Ghana da na 'yan majalissu.
BBCCopyright: BBC
Zaben shugaban kasar Ghana da 'yan majalissu
BBCCopyright: BBC
BBCCopyright: BBC
Abubuwan da aka yi yakin neman zabe
Batun tabarbarewar tattalin arziki da kuma cin hanci da rashawa su ne suka mamaye yakin neman zaben.
Tattalin arzikin kasar dai ya samu koma baya a 'yan shekarun nan.
Video content
Video caption: Halin da tattalin arzikin Ghana ke cikiHalin da tattalin arzikin Ghana ke ciki
Abubuwa biyar kan zaben Ghana da ya kamata ku sani
1. Masu suna John sune ke yawan shugabantar kasar
Tun shekarar 1992 masu suna John ne ke shugabantar kasar.
2. Tun shekarar 1992, jam'iyyu biyu ne kawai suka mamaye siyasar Ghana. Jam'iyyar National Democratic Congress ce ta shugaba mai mulki. Sai jam'iyyar New Patriotic Party ta hamayya.
3. A Duk lokacin da jam'iyyar Democrats ta lashe zaben shugaban kasar Amurka..... To sai ka ga Jam'iyyar NDC ma ta ci zabe a Ghana. Kuma idan Republican suka ci a Amurkan, haka ma jam'iyyar NPP ce ke lashe zaben Ghana.
4. A karon farko a tarihin, an samu mace ta farko Charlotte Osei, wadda ke shugabantar hukumar zaben kasar Ghana.
5. Ba a taba samun sauyin gwamnati a Ghana, ba tare da an yi zabe zagaye na biyu ba.
BBCCopyright: BBC
Charlotte Osei ce ke shugabantar hukumar da ke kula da zabe a GhanaImage caption: Charlotte Osei ce ke shugabantar hukumar da ke kula da zabe a Ghana
Mata masu ciki ba sa bin layin zabe
Mata masu ciki ba sa bin layi, ana basu dama su kada kuria da zarar sun je rumfar zabe.
BBCCopyright: BBC
An tantance mutane 99 a mazabar Zango B
Kawo yanzu mutane 99 sun kada kuria a mazabar Zango B, daga cikin mutane 639 kamar yadda wakilin BBC Yusuf Ibrahim Yakasai daga Kumasi a Ghana ya aiko mana da yadda ake tantance masu zabe.
Video content
Video caption: Tun da sanyin safiyar Laraba aka fara kada kuri'aTun da sanyin safiyar Laraba aka fara kada kuri'a
An tsaurara matakan tsaro a Tamale
Wakilin BBC Thomas Naadi ya wallafa hoto a Twitter da ke nuna jami'an tsaro suna sa-ido kan yadda al'amura ke tafiya a yankin Tamale.
Tuni wasu yan kasar ta Ghana suka kada kuri'un su kuma suka koma wajen sana'o'in su
BBCCopyright: BBC
Yadda ake tantace mutane a mazabar Zango B
Yusuf Ibrahim Yakasai
BBC Hausa, Kumasi, Ghana
Video content
Video caption: Tun da safiyar Laraba aka fara yin zabe a GhanaTun da safiyar Laraba aka fara yin zabe a Ghana
Wakilin BBC ya kada tasa kuri'ar
Daya daga cikin ma'aikatan BBC, Akwasi Sarpong, wanda dan kasar ta Ghana ne, kuma a yanzu yana can domin aiko da rahotanni kan zaben, shi ma ya kada tasa kur'ar:
Rahoto kai-tsaye
Daga Mohammed Abdu
time_stated_uk
Nan muka kawo karshen shirin sai an jiman ku.
An rufe rumfunan zaben kasar Ghana
An rufe kada kuri'a a zaben kasar Ghana, wanda aka yi na zaben shugaban kasa da na 'yan majalisa na shekarar 2016.
Ana yin zabe cikin kwanciyar hankali a Tamale
Thomas Naadi
BBC Africa, Accra
Ana gudanar da zabe a Tamale da ke Arewacin Ghana cikin kwanciyar hankali.
Ba a dai samu labarin barkewar rikicin siyasa ba.
Watakila saboda jami'an tsaro da ke yin sintiri a ciki da wajen birnin ne.
Yadda ake yin zabe a birnin Kumasi
Video content
'Yan takarar shugaban kasa masu amsa Nana sun yi zabe
'Yan takarar shugabancin kasar Ghana masu amsa sunan Nana sun kada kuri'arsu a zaben da ake gudanarwa.
Daya namiji ne mai amsa sunan Nana Akufo-Addo, shugaban jam'iyar New Patriotic Party, wanda ya yi zabe a birnin Accra.
Dayar kuwa mace ce mai suna Nana Konadu Agyeman-Rawlings mai takara a jam'iyar National Democratic Party.
Ana karfafa tsaro a lokacin da ake yin zabe
Jami'an tsaro da suka hadar da sojoji da yan sanda na ci gaba da sintiri a birnin Kumasi domin tabbatar da tsaro
Babu mutane da yawa a mazabar Malaga
Yusuf Ibrahim Yakasai
BBC Hausa, Kumasi, Ghana
A wasu mazabun ba mutane kamar mazabar Malaga.
To amma a wasu wuraren akwai masu zabe da yawa, kamar mazabar Malam Dudu akwai mutane da dama a kan layi.
Kuma babban Jami'in mazabar ya shedawa BBC cewa yana fargabar da wuya za su kammala da masu zabe kafin lokacin da za a kammala kada kuri'a.
Yadda ake zabe da harkar kasuwanci a mazabar Sawaba
Ibrahim Isa BBC Hausa Accra, Ghana
Video content
Fursunoni a Ghana na yin zabe a kasar
Fursunoni suna daga cikin masu kada kuri'a a zaben sugaban kasar Ghana da na 'yan majalissu.
Wannan shi ne karo na biyu da fursunonin ke yin zabe, bayan wanda suka yi a shekarar 2012.
A cewar wata kafar yada labarai da ke Ghana City FM a labarin da ta wallafa a shafinta na Intanet ta ce kimanin fursunoni 2,276 ne aka yi wa rijistar yin zabe a kasar ta Ghana.
Bin layi domin kada kuri'a
Jami'an zabe na taimakawa masu kada kuri'a hawa kan layi da bin ka'ida a wata mazaba da wakilin BBC Akweasi Sarpong ya ziyarta a birnin Accra:
Yawan mutanen da za su yi zabe
Ana kada kuri'a ne a mazabu dubu ashirin da takwas da dari tara da casa'in da biyu.
Haka kuma mutum miliyan goma sha biyar da dubu dari bakwai da uku, da dari tara da casain ne za su kada kuria a zaben shugaban kasar Ghana da na 'yan majalissu.
Zaben shugaban kasar Ghana da 'yan majalissu
Abubuwan da aka yi yakin neman zabe
Batun tabarbarewar tattalin arziki da kuma cin hanci da rashawa su ne suka mamaye yakin neman zaben.
Tattalin arzikin kasar dai ya samu koma baya a 'yan shekarun nan.
Video content
Abubuwa biyar kan zaben Ghana da ya kamata ku sani
1. Masu suna John sune ke yawan shugabantar kasar
Tun shekarar 1992 masu suna John ne ke shugabantar kasar.
2. Tun shekarar 1992, jam'iyyu biyu ne kawai suka mamaye siyasar Ghana. Jam'iyyar National Democratic Congress ce ta shugaba mai mulki. Sai jam'iyyar New Patriotic Party ta hamayya.
3. A Duk lokacin da jam'iyyar Democrats ta lashe zaben shugaban kasar Amurka..... To sai ka ga Jam'iyyar NDC ma ta ci zabe a Ghana. Kuma idan Republican suka ci a Amurkan, haka ma jam'iyyar NPP ce ke lashe zaben Ghana.
4. A karon farko a tarihin, an samu mace ta farko Charlotte Osei, wadda ke shugabantar hukumar zaben kasar Ghana.
5. Ba a taba samun sauyin gwamnati a Ghana, ba tare da an yi zabe zagaye na biyu ba.
Mata masu ciki ba sa bin layin zabe
Mata masu ciki ba sa bin layi, ana basu dama su kada kuria da zarar sun je rumfar zabe.
An tantance mutane 99 a mazabar Zango B
Kawo yanzu mutane 99 sun kada kuria a mazabar Zango B, daga cikin mutane 639 kamar yadda wakilin BBC Yusuf Ibrahim Yakasai daga Kumasi a Ghana ya aiko mana da yadda ake tantance masu zabe.
Video content
An tsaurara matakan tsaro a Tamale
Wakilin BBC Thomas Naadi ya wallafa hoto a Twitter da ke nuna jami'an tsaro suna sa-ido kan yadda al'amura ke tafiya a yankin Tamale.
Post update
Wasu sun kada kuri'a sun koma gida
Yusuf Ibrahim Yakasai
BBC Hausa, Kumasi, Ghana
Tuni wasu yan kasar ta Ghana suka kada kuri'un su kuma suka koma wajen sana'o'in su
Yadda ake tantace mutane a mazabar Zango B
Yusuf Ibrahim Yakasai
BBC Hausa, Kumasi, Ghana
Video content
Wakilin BBC ya kada tasa kuri'ar
Daya daga cikin ma'aikatan BBC, Akwasi Sarpong, wanda dan kasar ta Ghana ne, kuma a yanzu yana can domin aiko da rahotanni kan zaben, shi ma ya kada tasa kur'ar: