'Yan Afrika ta Kudu 84 ne suka mutu a Lagos

Asalin hoton, BBC World Service
Mujami'ar TB Joshua na da mabiya sosai a ciki da wajen Najeriya
Yawan 'yan kasar Afrika ta Kudu da suka mutu a masaukin bakin mujami'ar TB Joshua da ya rushe a jihar Lagos a Nigeria sun karu zuwa 84.
An dai yi amanna cewa 'yan Afrika ta Kudu da ke cikin ginin a lokacin da ya rushe sun kai 349.
Rahotanni sun ambato Jakadan Afrika ta Kudu a Najeriyar na cewa akwai yiwuwar yawan wadanda suka mutu ya zarta hakan.
A ranar Juma'ar da ta gabata ne katafaren ginin masaukin bakin ya rushe a jihar Lagos da ke kudancin Najeriya.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, MINTI ƊAYA DA BBC NA YAMMA 21/01/2021, Tsawon lokaci 1,01
MINTI ƊAYA DA BBC NA YAMMA 21/01/2021