Kungiyar ma'aikatan mai ta janye yajin aiki

Asalin hoton, AFP
Ministar mai ta Najeriya Alison Madeukwe
Ma'aikatan man fetur a Nijeriya da suka hada da 'ya'yan kungiyar NUPENG da PENGASSAN, sun janye yajin aikin da suka shafe kwanaki hudu suna yi a duk fadin kasar .
Kungiyoyin sun janye yajin aikin ne bayan da suka cimma matsaya da gwamnatin kasar a taron da suka yi a jiya akan harkar fansho na ma'aikatan kamfanin NNPC da kuma bukatar kyautata yanayin matatun man fetur na kasar.
Kungiyoyin sun ce gwamnatin kasar ta samin da biya da dama daga cikin bukatunsu.
A halin yanzu Nijeriya na sayo akasarin albarkatun man fetur dinta ne daga kasashen waje saboda matatun man fetur na kasar basa aiki yadda yakamata
Abin da wasu masu sharhi kan tattalin arziki suka ce na janyo illa ga tattalin arzikin kasar
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti Daya Da BBC Safe 18/01/2021, Tsawon lokaci 1,00
Minti Daya Da BBC Safe 18/01/2021