Scotland ta yi watsi da 'yancin kai

Asalin hoton, Reuters
Scotland ta ce a'a
Yankin Scotland ya ka da kuru'ar ci gaba da zama a hadaddiyar daular Birtaniya, inda ya yi watsi da samun 'yancin kai da kashi goma cikin dari.
Jama'a masu dumbin yawa ne suka fito domin kada kuru'arsu a zaben raba gardamar da aka yi.
Masu yakin neman a ci gaba da zama tare sun samu nasara a yankunan da masu neman 'yanci suka yi zaton za su samu gagarumin goyon baya.
Shugaban masu neman a zauna tare, Alistair Darling, ya ce mutanen yankin Scotland sun zabi sauyi mai ma'ana a madadin rabuwar da ba'a bukata.
A lokacin da ya ke amincewa da shan kaye, minista na daya na yankin Scotland, Alex Salmond, ya ce kuru'ar ta nuna akwai gagarumin goyon baya na samun 'yan cin kai a nan gaba.
Amma Firayi Ministan Birtaniya, David Cameron, ya ce a yanzu an daidaita wannan magana baki dayanta a wannan takin.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, MINTI ƊAYA DA BBC NA RANA 19/01/2021, Tsawon lokaci 1,04
MINTI ƊAYA DA BBC NA RANA 19/01/2021