Ebola: Saliyo ta kafa dokar hana fita

Asalin hoton, AP
Majalisar dinkin duniya ta ayyana cutar Ebola a matsayin babban kalubale na tsaro da zaman lafiya
Kasar Saliyo ta sanya dokar hana fita na tsawon kwanaki uku a yunkurin da takeyi na kawo karshen yaduwar cutar Ebola.
Dokar ta fara aiki ne a ranar Juma'a kuma za ta kare a ranar Lahadi mai zuwa, kuma a tsawon kwanakin jami'an sa kai za su bi gida-gida don gano masu dauke da cutar Ebola.
Haka kuma za a yi amfani da wannan dama wajen wayar da kan daukacin 'yan kasar miliyan shida a kan cutar, tare da raba musu sabulai.
Gwamnatin Saliyo ta ce akwai bukatar daukar kwararan matakai domin kawo karshen cutar ebola a kasar.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti Ɗaya Da BBC Na Rana 22/01/2021, Tsawon lokaci 1,09
Minti Ɗaya Da BBC Na Rana 22/01/2021