Masallacin da ke maraba da 'yan luwadi a Afrika ta Kudu

Asalin hoton,
Taj Hargey ya ce bai sabawa koyarwar musulunci ba
Wani Musulmi malamin jami'a ya bude wani Masallaci a kasar Afirka ta Kudu, wanda ya baiwa 'yan luwadi damar zuwa su yi sallah a masallacin.
Taj Hargey, ya ce Masallacin, wanda aka gina shi a Cape Town, yana maraba da kowa da kowa ba tare da la'akari da bambancin jinsi ko addini ba.
Taj Hargey, wanda Furofesa ne a cibiyar Nazarin Addinin Musulunci a jami'ar Oxford da ke Birtaniya ya shaida wa BBC cewa kowa na iya limanci a masallacin, har da Mata, don maza da mata na iya shiga sahu guda.
A yanzu haka, Furofesan na fuskantar barazanar kisa daga al'ummar da ke yankin.
Kungiyoyin Musulmi a kasar Afirka ta Kudu da kuma Majalisar shari'ar Addinin Musulunci ta kasar sun ce suna gudanar da bincike a kan sabon masallacin, kuma suna sane da korafin da al'ummar Musulmi ke yi a kansa.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti daya da BBC Safe 20/01/2021, Tsawon lokaci 1,14
Minti Ɗaya da BBC na Safiyar 20/01/2021 wanda Sani Aliyu da Nabeela Mukhtar Uba su ka karanto.