Ebola: Ana son a jinkirta bude makarantu
A Najeriya, kungiyar malamai ta kasar ta bukaci gwamnati da ta kara jinkirta batun komawar dalibai makaranta saboda cutar Ebola.
A ranar Litinin ne dai aka tsara dalibai za su koma makaranta, bayan dogon zaman da suka yi a gida, don hana yaduwar Ebola, wadda ta bulla a kudancin kasar.
Shugaban kungiyar malaman ya ce babu wani tanadi kariya da aka yi a makarantun.
Sai dai Shugaban Najeriyar, Goodluck Jonathan, ya yi watsi da kiran da kungiyar malaman ke yi.
Amma wasu jihohin da kuma wasu makarantu masu zaman kansu a kasar sun ce za su jinkirta komawar daliban.
A da dai gwamnatin tarayya ta ce ba za a bude makarantun ba har sai tsakiyar watan Oktoba, amma daga baya ta takaita lokacin, ta ce a koma a ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, bayan da ta lura cewa matsalar cutar Ebolar ta ragu sosai a kasar.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti Ɗaya Da BBC Na Rana 22/01/2021, Tsawon lokaci 1,09
Minti Ɗaya Da BBC Na Rana 22/01/2021