'An shawo kan Ebola a Nigeria da Senegal'

Asalin hoton,
Mutane 2,800 ne suka mutu sakamakon kamuwa da cutar Ebola
Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce an shawo kan barkewar cutar Ebola a kasashen Nigeria da Senegal cikin kasashe biyar da cutar ta bulla a yammacin Afirka.
Amma WHO ta ce gabaki-dayan yawan mutanen da suka mutu sun karu zuwa kusan mutane 2,800.
A Kasar Saliyo, Shugaban cibiyar ayyukan gaggawa akan cutar Ebolan Stephen Gaojia ya ce an sami nasarar shawo kan cutar bayan da aka kawo karshen dokar hana fitar da aka sanya a Kasar a ranar Lahadi.
Hukumomin Kasar Saliyo sun sami mutane 130 dake dauke da cutar a lokacin da dokar ke aiki.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, MINTI ƊAYA DA BBC NA YAMMA 21/01/2021, Tsawon lokaci 1,01
MINTI ƊAYA DA BBC NA YAMMA 21/01/2021