Omar al-Bashir ya rusa gwamnatinsa

Shugaba Albashir ya lashe takobin farfado da tattalin arzikin Sudan

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto,

Shugaba Albashir ya lashe takobin farfado da tattalin arzikin Sudan

Shugaban Sudan Omar al-Bashir ya rusa gwamnatinsa, inda yake cewa kokari ne na shawo kan matsalar tattalin arzikin kasar.

Za kuma a rage adadin yawan ministocin daga 31 zuwa 21.

Shugaba al-Bashir ya ce daukan wannan mataki ya zama tilas domin magance radadi da wahalhalu da kasar ke fuskanta.

Wakilin BBC ya ce: 'Tattalin arzikin Sudan na cikin matsala, kuma kasar na fuskantar haka ne tun bayan balewar Sudan ta kudu daga kasar a 2011, wadda ta yi gaba da kaso mai yawa na albarkatun man kasar.'

Tun a watan Janairu Sudan ke fuskantar zanga-zanga, lokaci da farashin burodi ya rubanya, bayan gwamnatin Sudan ta soke tallafin da take bayarwa a kansa.

Darajar kudin kasar kuma ya karye, wanda hakan ya sa a ke wahala sosai wajen iya sayen kayayyakin amfani daga kasashen ketare.