Manchester City ta ci Manchester United a gida

Asalin hoton, Getty Images
Jose Mourinho da Guardiola suna tafawa kan nasarar Man City
Manchester City ta samu nasara a kan Manchester United da ci 2-1, a wasan da suka buga ranar Asabar, a Old Trafford.
Dan wasan Man City, Kevin de Bruyne ne ya fara jefa kwallon farko a ragar Man United.
Kelechi Iheanacho ne kuma ya sanya kwallo ta biyu, a inda shi kuma Zlatan Ibrahimovic ya ci wa Man United kwallo daya.
Yanzu dai Manchester City tana da maki 12 kuma ita ce a saman teburin gasar Premier, bayan da ta samu nasara a wasanninta dari bisa dari.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti daya da BBC Safe 20/01/2021, Tsawon lokaci 1,14
Minti Ɗaya da BBC na Safiyar 20/01/2021 wanda Sani Aliyu da Nabeela Mukhtar Uba su ka karanto.