An raba jadawalin cin kofin Afirka a kwallon mata

Afirka

Asalin hoton, Google

Bayanan hoto,

Kamaru ce za ta karbi bakuncin gasar cin kofin Afirka karo na 10 a kwallon kafa ta mata

Hukumar kwallon kafa ta Afirka, Caf, ta raba jadawalin wasan cin kofin nahiyar Afirka a kwallon kafa ta mata.

Gasar da za a yi karo na 10, ta kunshi kasashe takwas a jadawalin da aka fitar a ranar Lahadi a Yaounde, Kamaru.

Rukunin farko ya kunshi mai masaukin baki Kamaru da Masar da Afirka ta Kudu da kuma Zimbabwe.

Nigeria da Mali da Ghana da kenya suna rukuni na biyu.