Manchester City za ta karbi bakuncin Barcelona

Champions Leagu

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,

Barcelona ce ta daya a kan teburin rukuni na uku

Manchester City za ta karbi bakuncin Barcelona a gasar cin Kofin Zakarun Turai wasa na biyu da za su fafata a Ettihad a ranar Talata.

A wasan farko da suka yi a Camp Nou, Barcelona ce ta shararawa City kwallaye 4-0, kuma Messi ne ya ci uku a karawar, Neymar ya ci guda daya.

Barcelona ce ke mataki na daya a kan teburin rukuni na uku da maki tara, sai Man City ta biyu da maki hudu, sannan Borussia Monchengladbach da maki uku, Celtic da maki daya.

Haka kuma a ranar ta Talata Borussia Monchengladbach za ta karbi bakuncin Celtic a Jamus.