Liverpool ta ci gaba da zama ta biyu a kan teburin Premier

Asalin hoton, Getty Images
Kwallo na biyu da Wijnaldum ya ci wa Liverpool a bana
Liverpool ta ci gaba da zama a mataki na biyu a kan teburin Premier, bayan da ta doke Manchester City 1-0 a wasan mako na 19 da suka fafata a Anfield a ranar Asabar.
Liverpool ta ci kwallon ne tilo ta hannun Georginio Wijnaldum a minti na takwas da fara tamaula, wanda hakan ya sa ta hada maki uku a karawar.
Da wannan nasarar Liverpool ta yi wasanni 17 a Anfield ba tare da an samu nasara a kanta ba.
Haka kuma kungiyar ta kafa tarihin hada maki 43 a wasanni 19 da ta buga a gasar Premier, bayan da ta taba hada maki 42 a kakar wasan 2008/09.
Liverpool za ta ziyarci Sunderland a wasan mako na 20, yayin da Manchester City za ta karbi bakuncin Burnley.
Babban Labari
Minti Daya Da BBC
Saurari, Minti Ɗaya Da BBC Na Rana 22/01/2021, Tsawon lokaci 1,09
Minti Ɗaya Da BBC Na Rana 22/01/2021