Liverpool ta yi rashin nasara kan daukaka karar Mane

Asalin hoton, Rex Features
An fitar da Sadio Mane a zagaye na farko na wasan
Liverpool ta yi rashin nasara kan daukaka karar rage wa'adin haramcin da aka yi wa Sadio Mane a wasan da Manchester City ta doke su da ci 5-0.
An kori Mane, mai shekarar 25, daga fili minti 37 da soma wasa bayan ya shuri mai tsaron ragar City Ederson a fuska da kafa.
Dan wasan dan kasar Senegal ba zai buga wasan Premier League da za su yi da Burnley da Leicester ba, da kuma wasan da za su yi a gidan Leicester na cin kofin EFL.
Liverpool za ta buga wasan cin kofin zakarun Turai da Sevilla a ranar Laraba a Anfield.