'Yan PSG da suka je Man City buga Champions League

Champions League

Asalin hoton, Getty Images

Manchester City za ta karbi bakuncin Manchester City a wasa na biyu na daf da karshe a Champions League da za su fafata ranar Talata a Etihad.

A wasan farko da suka buga a Faransa ranar 28 ga watan Afirilu, City ce ta yi nasara da ci 2-1.

Wannan shi ne wasa na biyar da za su fafata a tsakaninsu a gasar Zakarun Turai, inda City ta yi nasara a biyu da canjaras biyu.

City wadda take ta daya a teburin Premier ta lashe Caraboa Cup na bana na hudu a jere kuma na takwas jumulla.

Paris St Germain tana ta biyu a kan teburin Ligue 1 da maki 75 da tazarar maki daya tsakaninta da Lille wadda ke jan ragama.

Wannan ne karon farko da Pep Guardiola ya kai wannan matakin a Champions League a Manchester City, wadda ba ta taba lashe kofin ba.

A bara PSG ta kai karawar karshe a Champions League, inda ta yi rashin nasara da ci 1-0 a hannun Bayern Munich.

'Yan wasan Paris St Germain:

  • BAKKER Mitchel
  • DAGBA Colin
  • DIALLO Abdou
  • DI MARIA Angel
  • DRAXLER Julian
  • FLORENZI Alessandro
  • GUEYE Idrissa (an dakatar da shi, amma an je da shi Faransa)
  • HERRERA Ander
  • ICARDI Mauro
  • KEAN Moise
  • KEHRER Thilo
  • KIMPEMBE Presnel
  • KURZAWA Layvin
  • MARQUINHOS
  • MBAPPÉ Kylian
  • NAVAS Keylor
  • NEYMAR JR
  • PAREDES Leandro
  • PEREIRA Danilo
  • RAFINHA
  • RANDRIAMAMY Mathyas
  • RICO Sergio
  • SAIDANI Yanis
  • SARABIA Pablo
  • VERRATTI Marco

Wadan da ke jinya:

  • BERNAT Juan
  • FRANCHI Denis
  • GHARBI Ismael
  • KAMARA Abdoulaye
  • LETELLIER Alexandre
  • MICHUT Edouard
  • NAGERA Kenny
  • PEMBÉLÉ Timothée
  • SIMONS Xavi